'Yan awaren Kamaru sun jefa matafiya cikin kasada – DW – 09/17/2024
  1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaAfirka

'Yan awaren Kamaru sun jefa matafiya cikin kasada

Zakari Sadou SB
September 17, 2024

Matuka motoci a yankin kudu maso yammacin Kamaru sun koka da dokar hana fita da 'yan aware suka wadda ta shafi motocin sufuri da manyan motocin dakon kaya gami da dalibai yayin komawa sabon zangon karatu a kasar.

https://p.dw.com/p/4kjHQ
Motocin Tasi a Kamaru
Motocin Tasi a KamaruHoto: Thomas Imo/photothek/picture alliance

Matuka motocin sun tsayar da jigirlar matafiya da dakon kaya a yankin tsak sakamakon barazanar 'yan bindiga wanda daya daga cikin matuka motocin ya shaida wa DW cewa ya yi asarar motarsa guda a 2019 da 'yan bindiga suka kona kurmus sakamakon rashin mutunta dokar da suka sanya ta tilasta zaman gida da hana zirga-zirgar ababen hawa a fadin yankin.

Karin Bayani: Najeriya: Harin 'yan Ambazoniya na Kamaru

Yanzu haka motocin sufuri da dama na ajiye sun cika wajen ajiye motoci da ke tashar na zuwa kudu maso yammaci a garin Bonaberi karamar hukumar Douala na hudu. Wannan babbar matsala ce ga direbobin saboda ba su da wata hanyar shigar kudi duba da abubuwa da ke kansu kamar inshora da biyan haraji da sauransu ga hukuma.

Motocin Tasi a Kamaru
Motocin Tasi a KamaruHoto: Ahmet Emin Donmez /Anadolu/picture alliance

Baya ga direbobin motocin sufuri na fasinja, manyan kamfanoni kamar CDC na ayyukan noma sun rage direbobin manyan motocin dakon kaya sakamakon barazanar 'yan bindigan domin a shekarar 2022 yan awaren sun yi awon gaba da direbobin kamfanin guda 8 lokacin da suke kan hanyarsu tsakanin garin Tiko da Douala cibiyar kasuwancin Kamaru.

Tattalin arzikin kasar ya durkushe sosai sakamakon rikici tsakanin dakarun Yaounde da 'yan aware da suka dauki makamai a 2017 domin kafa kasarsu mai cin gashin kanta sai dai a hanlin yanzu rikici ya canza salo saboda fararen hula 'yan awaren da jami'an tsaron ke musgunawa mafi yawan mutanen da suka mutu fararen hula dubbai kuma sun yi gudun hijira zuwa sassan kasar musamman ma Douala.