Masar ta kori kocinta – DW – 09/06/2021
  1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta kori kocinta

Abdul-raheem Hassan
September 6, 2021

Hukumar kwallon kafa ta Masar ta kori kocinta Hossam al-Badry kwana guda bayan da 'yan wasan kasar ta yi canjaras da 'yan wasan Gabon a wasan neman shiga gasar cin kofin duniya na 2022 da za a kara a aksar Katar.

https://p.dw.com/p/3zzpO
Algerien - Ägypten / WM-Qualifikation / Fußball
Hoto: AP

Ana kuma sa ran sanar da sabon kocin da zai cigaba da jan ragamar 'yan wasan na Masar nan na kwanaki biyu. Wasan raunin da Masar ta yi da Gabon a ranar Lahadin da ta gabata, inda suke bukatar dai-daita minti na 90 don kubutar da maki daya, da kuma nasarar da suka samu da ci 1-0 a kan Angola a wasan share fagen shiga gasar cin kofin duniya da suka gabata, ya haifar da suka mai zafi daga magoya bayan da ba su ji dadi ba a shafukan sada zumunta.